Najeriya ce ta uku da aka fi fama da ta'addanci a duniya





Wani rahoton hukumomin kasa da kasa kan ayyukkan ta'addanci ya ce Najeriya ce ta uku cikin jerin kasashen da suka fi fama da ta'addanci a duniya.
Rahoton wanda cibiyar bunkasa tattalin arziki da zaman lafiya ta IEP da ke birnin Sydney ta fitar ya nuna cewa bayan kasashen Iraqi da Afghanistan, Najeriya ce a kan gaban wajen yawan mutanen da suka mutuwa saboda hare-haren da ke da alaka da ta'addanci.
Sai dai rahoton ya ce an samu raguwar yawan adadin mutanen da suka mutu sakamakon hare-haren ta'addanci idan aka kawatanta da shekarar 2018.
Amma kuma rahoton ya ce ta'addanci na ci gaba da yaduwa a kasashe.
A cewar rahoton, a Najeriya an kai hare-haren ta'addanci 562 da suka kashe mutum 2,040, adadin da ya kai kasar matsayi na uku a jerin kasashen da ke fama da hare-haren ta'addanci.
Afghanistan ce ta daya a duniya da aka fi fama da hare-haren ta'addanci inda aka kai hare-hare 1,443 da suka kashe mutum 7,379, sai Iraqi da aka halaka mutum 1,054 a hare-hare 1,131.
Hakan nafin an fi kai hare hare a Najeriya fiye da Syria da ke matsayi na hudu inda aka kashe mutum 662 a hare-hare 131 na ta'addanci.
A nahirar Turai, inda rahoton ya ce ba a fuskanci hare-haren ta'addanci ba a 2018, adadin wadanda suka mutu ya ragu daga 200 zuwa 62.

(c) BBC Hausa

Comments

Popular posts from this blog

An Urgent Call to Authorities on Graduation Celebrations

ADC Begins Distribution of Membership Cards, Registers Across 14 LGAs

ADC Dansadau Ward Holds Stakeholders’ Meeting Under Hon. Ahmad Abubakar Milo